Isa ga babban shafi

Gbagbo ya bayyana aniyarsa ta sake neman shugabancin Cote d'Ivoire

Tsohon shugaban kasar Ivory Coast, Laurent Gbagbo ya amince ya yi wa jam'iyyarsa takaran neman shugaban kasa a zaben 2025.

Tsohon shugaban kasar Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo uyayin jawabi ga manema labaru a Abidjan 22/08/23.
Tsohon shugaban kasar Cote d'Ivoire Laurent Gbagbo uyayin jawabi ga manema labaru a Abidjan 22/08/23. AFP - SIA KAMBOU
Talla

Katinan Kone, kakakin jam'iyyar African People's Party - Cote d'Ivoire wanda Gbagbo ya kafa a shekarar 2021 ne ya sanar da matakin bayan wani taro da kwamitin koli na jam'iyyar ya gudanar a ranar Asabar.

A shearer 2021 ne Gbagbo ya kuma gida bayan da Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) ta wanke shi daga zargin hannu a yakin basasar kasar na shekarar 2019 sakamakon kin amincewa da shan kaye a zaben 2010.

Jam'iyyarsa ta farko

Ya rasa iko da jam'iyyar da ya kafa a baya, wato Ivory Coast Popular Front (IPF), yayin da yake zaman kurkuku yana jiran shari'a a Netherlands tsawon shekaru da dama, amma har yanzu yana riƙe da manyan magoya bayansa da ya amince a gida.

Ana sa ran gudanar da zaben kasar da ke yammacin Afirka a watan Oktoba na shekarar 2025. Shugaba Alassane Ouattara, mai shekaru 82, wanda aka sake zaba a shekara ta 2020 bai bayyana ko zai sake tsayawa takara ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.