Isa ga babban shafi

Kasashen Afirka na taro kan yadda za a kawar da cutar Malaria daga nahiya

Ministocin lafiya daga kasashen Africa 12 da suka fi fama da matsalar cutar zazzabin cizon sauro sun yi wata ganawa ta musamman a birnin Yaounde na kasar Kamaru.

Taron ya gudana ne a birnon Yaounde na kasar Kamaru.
Taron ya gudana ne a birnon Yaounde na kasar Kamaru. © WHO
Talla

Taron nasu na da nufin gano hanyoyin da za’a bi wajen magance illolin cutar da kuma yadda za’a yi amfani da hanyoyi na zamani don kawo karshenta.

Da yake jawabi, ministan lafiyar kasar Mali, Assa Badiallo ya ce babu wata kasa da zata iya magance matsalar cutar la’akari da tasirin ta, amma da hadin kai, cutar ka iya zama tarihi cikin dan kankanin lokaci.

Kaso 70 cikin 100 na mace-macen da ake samu dalilin cutar malária na faruwa ne a kasashen Africa musamman Burkina Faso, Cameroon, Jamhuriyar dimokradiyyar  Congo, Ghana, Mali, Mozambique, Niger, Nigeria, Sudan, Uganda da Tanzania.

Kididdiga ta nuna cewa cutar na kashe mutane akalla dubu daru 6 kowacce shekara a Nahiyar Africa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.