Isa ga babban shafi

Shugaban Senegal ya yi alkawarin gudanar da zabe da wuri-wuri

Shugaban kasar Senegal Macky Sall, wanda ke fuskantar matsananciyar matsin lamba a cikin gida da wajen kasar, ya sha alwashin shirya zaben shugaban kasa da wuri-wuri, bayan da da majalisar tsarin mulkin kasar ta yi watsi da matakin da ya dauka na jinkirta zaben na wannan wata.

Mack Sall Shugaban kasar Senegal
Mack Sall Shugaban kasar Senegal © AP/Christophe Ena
Talla

Yunkurin da Shugaban na Senegal ya yi na dage zaben ranar 25 ga watan Fabrairu har zuwa Disamba ya janyo rikici cikin kasar ta Senegal mafi muni cikin shekaru da dama.

Matakin dai ya haifar da cece-kuce da zanga-zangar da ta yi sanadiyar mutuwar mutane.

Hukuncin da majalisar tsarin mulkin kasar ta yanke ranar Alhamis na soke jinkirin zaben ya jefa kasar cikin rashin tabbas.

Shugaban kasar ya kuduri aniyar aiwatar da cikakken hukuncin majalisar tsarin mulkin kasar,” in ji fadar shugaban kasar a cikin wata sanarwa.

Masu zangan-zanga a kasar Senegal
Masu zangan-zanga a kasar Senegal REUTERS - ZOHRA BENSEMRA

"Don haka, ba tare da bata lokaci ba, shugaban kasar zai gudanar da shawarwarin da suka dace don shirya zaben shugaban kasa da wuri-wuri."

Macky Sall, wanda ke kan karagar mulki tun a shekarar 2012, ya ce ya dakatar da zaben da za a yi a wannan watan ne saboda takaddamar da ake yi game da soke zaben da ake yi da ‘yan takara da kuma nuna damuwa kan komawar tarzoma da ake gani a 2021 da 2023.

Shugaban kasar Senegal Macky Sall
Shugaban kasar Senegal Macky Sall AFP - AMANUEL SILESHI

Daga baya majalisar ta amince da jinkirin zuwa ranar 15 ga watan Disamba, amma sai bayan da jami’an tsaro suka shiga ginin tare da cire wasu ‘yan adawa a cikin majalisar.

Kuri'ar ta share fagen wa'adin Sall -- wanda wa'adinsa na biyu zai kare a watan Afrilu,ya ci gaba da zama kan karagar mulki har sai an girka magajinsa.

Masu zanga-zanga a kasar Senegal
Masu zanga-zanga a kasar Senegal © JOHN WESSELS / AFP

An kashe mutane uku a yayin zanga-zangar nuna adawa da jinkirin kada kuri’a, inda jami’an tsaro suka dakile yunkurin gangamin.

Mutane kalilan ne suka amsa kiran zanga-zangar da aka yi a Dakar babban birnin kasar a jiya.

'Yan adawar dai sun yi Allah wadai da matakin na Shugaba Sall a matsayin wani juyin mulki na kundin tsarin mulkin kasar, inda suka ce jam'iyyarsa na fargabar shan kaye a akwatin zabe na dan takararta, Firayiminista Amadou Ba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.