Isa ga babban shafi

Nijar da Mali da Burkina sun kulla yarjejeniyar yaki da ta'addanci

Jagororin gwamnatin sojin kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar sun kulla wata yarjejeniyar yaki da ‘yan ta’addda  masu ikirarin jihadi tare da samar da hadin-kai ta fanni siyasa a tsakaninsu a kokarin da suke na maido da matabar kasashensu.

Shugaban gwamnatin sojin Nijar Janar Abdorahmane Tianni tare da Kanar Assimi Goita a Mali
Shugaban gwamnatin sojin Nijar Janar Abdorahmane Tianni tare da Kanar Assimi Goita a Mali © Niger Presidency
Talla

Dukkannin kasashen 3 sun fuskanci juyin mulki tun daga shekarar 2020, sakamakon matsalar tsaro da suka samo asali daga ayyukan ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi, wadanda suka taso daga arewacin Mali a shekarar 2012, kana daga bisani suka bazu zuwa Nijar da Burkina Faso.

Bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a Jamhuriyar Nijar ne kugiyar ECOWAS ta kakaba wa kasar takunkumai,  bayan barazanar amfani da karfin soji da ta yi a kan masu  juyi mulkin, tana mai bukatar maido da mulkin dimokaradiyya cikin hanzari.

Sakamakon haka ne a  watan Satumba, Mali da Burkina da Nijar  suka kulla kawance da zummmar taimaka wa juna ta bangaren soji idan batun kai wa wani daga cikinsu hari ya tabbata.

Juyin mulkin Mali da Jamhuriyar Nijar da Burkina sun haddasa lalacewar danngantaka tsakaninsu da tsohuwar uwargijiyarsu Faransa, inda suka karkata zuwa Rasha.

Sai dai a yayin da wannan sabuwar dangantaka da aka kulla ta ta’allaka ga tsaro ne kawai, shugaban mulkin sojin Burkina  Faso, Kanar Ibrahim Traore ya ce ana iya fadadawa ta shafi tattalin arziki da sauransu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.