Isa ga babban shafi

Cutar kwalara ta kashe mutane 5 a Kamaru

Annobar cutar amai da gudawa da ta barke a birnin Younde na Kamaru ta hallaka mutane biyar kawo yanzu, a cewar ma’aikatar lafiyar kasar, wadda kuma tayi gargadi game da daukar matakan kare Yaduwar cutar. 

Taswirar Kamaru.
Taswirar Kamaru. © AFP
Talla

Ma’aikatar lafiyar kasar tace a yanzu akwai bayanin mutane 88 dauke da cutar tun farkon watan Maris zuwa yanzu kusan dukannin su a yankin Yaounde na kasar. 

Ministan Lafiyar kasar Manouda Malachie ta cikin wata sanarwa da ya fitar, a yanzu dukannin masu ruwa da tsakni a fannin lafiyar kasar na kan shrin ko ta kwana don shawo kan cutar. 

A bara dai cutar ta hallaka mutane 272, cikin mutane 12,952 da suka kamu a tsakanin shekara guda kachal. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.