Isa ga babban shafi

'Yan jaridar Kamaru 2 sun bukaci kariya daga barazanar kisan da ake musu

Wasu ‘yan jarida biyu a Kamaru, sun bukaci gwamnatin kasar da ta basu kariya, sakamakon barazanar kashe su da wani magajin gari ke yi, biyo bayan binciken kwakwaf din da suke gudanarwar akan zarginsa da hannu a a wata badakalar cin hanci da rashawa a wasu manyan ayyukan shimfida tituna da ya bayar.

Hoton fitacccen dan jaridar kasar Kamaru marigayi Martinez Zogo wanda aka sace aka kuma yi wa kisan gilla cikin watan Janairu na shekarar 2023.
Hoton fitacccen dan jaridar kasar Kamaru marigayi Martinez Zogo wanda aka sace aka kuma yi wa kisan gilla cikin watan Janairu na shekarar 2023. © REUTERS/Amindeh Blaise Atabong
Talla

‘Yan jaridar da ake zargin Magajin garin Maroua Sali Babani da yi wa barazana dai sun hada da Aminou Alioum wakilin kafar yada labaran Cchannnel 2 International da ke Douala, sai kuma Ousman Alhaji Boubakari.

‘Yan jaridun biyu sun ce an sha kiran wayoyinsu a lokuta da dama, tare da yi wa rayuwarsu barazana, muddin basu daina watsa rahotannin da ke caccakar magajin garin da suke bincike kan ayyukansa ba.

Wannan barazana na zuwa ne kasa da watanni uku, bayan kashe wasu manema labarai da aka yi cikin watan Janairun da ya gabata a kasar ta Kamaru, sakamakon ficen da suka yi wajen kkokarin bankado laifukan cin hanci da rashawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.