Isa ga babban shafi
Najeriya-Kaduna

El-Rufa'i ya sassauta dokar killace jama'a ta kwanaki 75

Gwamnan Jihar Kaduna da ke Najeriya Malam Nasir El Rufai ya sanar da dokar kawo karshen killace mutane da akayi a gida na kwanaki 75 domin yaki da annobar coronavirus daga gobe laraba.

Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa.
Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa. kdsg.gov.ng
Talla

A jawabin da ya yiwa al’ummar kasar ta kafar talabijin, El Rufai ya ce daga gobe laraba dokar hana fita za ta yi aiki ne kawai daga karfe 8 na dare zuwa 5 na asuba, yayin da jama’a za su cigaba da zirga-zirga a cikin Jihar.

Gwamnan ya ce za’a bai wa jama’a damar gudanar da sallar juma’a da addu’a a mujami’u ranakun lahadi kawai, yayin da ake bukatar jama’a su tabbatar da kiyaye dokokin bada tazara wanke hannu da kuma gwajin yanayin jikin mutuum.

El Rufai yace ma’aikata zasu koma bakin aikin su bisa ka’idodin da shugaban ma’aikatan Jihar zai gabatar nan gaba, yayin da za’a dinga bude ofisoshin gwamnati daga karfe 9 na safe zuwa 3 na yamma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.