Isa ga babban shafi
Guinea Conakry

An gano wasu mutane dauke da Ebola a Guinea

Gwamnatin kasar Guinea ta bayyana cewa an samu mutane biyu dauke da cutar Ebola bayan an yi musu gwaji.

Ebola ta sake bulla a kasar Guinea
Ebola ta sake bulla a kasar Guinea REUTERS/Daniel Berehulak/The New York Times/
Talla

Wannan na zuwa ne ‘yan sa’oi da hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce, babu sauran cutar a kasar Saliyo mai makwabtaka da Guinea.

Wani jami’in gwamnatin kasar ya ce, mutanen da suka kamu da cutar mazauna kauyen Korokpara ne, inda aka samu mutane uku 'yan gida daya da suka rasa rayukansu a 'yan makwannin da suka shude bayan sun yi ta amai da gudawa.

An yi amanna cewa, cutar ta Ebola ta fara bulla ne a kasar Guinea  yayin da ta kashe sama da mutane dubu 11 da 300 tun bayan barkewarta a shekarar 2013 a kasashen Liberia da Saliyo da Guinea.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.