Burundi
An Gurfanar da Sojan Burundi 18 Gaban Kotu
Gwamnatin shugaban Burundi Pierre Nkurunziza wanda ya tsallake rijiya da baya ta gabatar da wasu soja da aka kama, su 18 gaban kotu saboda yunkurin kifar da Gwamnati.Tun a jiya Asabar wasu dake bore sun bi tituna suna la'antar yunkurin shugaban kasar ta su na neman zarcewa da iko wa'adi na uku.Har ya zuwa yanzu ba’a san makomar Babban sojan da ya sanar da kifar da Gwamnati ba, wato Janar Godefroid Niyombare.Wasu majiyoyi na cewa mazauna birnin Bujumbura na shirin fitowa soisai domin bore saboda adawa da yunkurin shiugaban kasar na zarcewa da mul;ki.
Wallafawa ranar: