Mali
An harbe wani ma’aikacin Red Cross a Mali
Kungiyar Agaji ta Red Crosss ta ce an harbe wani ma’aikacinta a Mali lokacin da ‘yan bindiga suka bude wuta kan motar da ke dauke da kayan agaji. Kungiyar ta bayyana bakin-cikinta da harin da aka kai wa motar agajin a Gao da ke Arewacin kasar.
Wallafawa ranar:
Talla
Daraktan kungiyar mai kula da Yammaci da Arewacin Afirka Yasmine Praz Dessimoz, ta ce direban motar mai suna Hmaadoun na tuka motar ne daga Gao zuwa Nijar domin karbar kayan magani.
Har yanzu ba a tantance ‘Yan bindigar ba wadanda suka bude wa Motar Red Cross wuta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu