Isa ga babban shafi
Mali

An kashe sama da mutane 10 a harin kunar bakin Wake a kasar Mali

Wani harin da masu goyon bayan gwamnati da suka hada da ‘yan kunar bakin Wake suka kai a yankin Arewacin Mali, ya yi sanadin mutuwar sama da mutane 10 kai tsaye

Un blessé, soigné à l'hôpital de Gao, au Mali, le 27 janvier 2015.
Un blessé, soigné à l'hôpital de Gao, au Mali, le 27 janvier 2015. REUTERS/Stringe
Talla

Wata majiyar jami’an tsaro ta ce mayakan na GATIA ne tare da wasu ‘yan kunar bakin wake suka kai harin ga ‘yan tawaye masu adawa da gwamnatin kasar Larabawa a kusa da garin Tabankort.

Haka ma an ce an kashe wasu mutane 3 a wata zanga-zangar da aka yi ta kalubalantar Majalisar dunkin Duniya.

Wata majiyar jami’an tsaro a MINUSMA ta ce Rundunar Dakarun tsaro na Majalisar dunkin Duniya a Mali ta tabbatar da kisan, ta kara da cewar wasu mahara biyu sun tarwatsa kansu a yayin da aka kashe na 3 kamin ya iya tarwatsa kansa.

An dai tilastawa Dakarun Majalisar dunkin Duniya ficewa ne, a wani matakin kirkiro sansanin Jami’an tsaro na wuccin gadi a Tabankort, bayan wata yarjejeniya da aka yi a yankin Arewacin birnin bao, da aka ce wasu masu goyon bayan gwamnati suka shirya.

An kuma kashe wasu mutane 3 a ran Talata, rana ta 2 da aka gudanar da zanga-zangar kyamar Dakarun Majalisar dunkin Duniya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.