Isa ga babban shafi
Ebola

Kasashen Duniya na shirin daukar tsauraran matakai a kan cutar Ebola

Shugabannin kasashen Birtaniya, Amurka, Faransa, Jamus da kuma Italiya, sun bayyana cewa Ebola na a matsayin annoba mafi muni da duniya ta taba fuskanta a cikin shekarun baya bayan nan.

Tattaunawa a zauren MDD kan cutar Ebola
Tattaunawa a zauren MDD kan cutar Ebola REUTERS/Eduardo Munoz
Talla

Hakkan dai na zuwa ne bayan wata sanarwa da fadar firaministan Birtaniya david Cameron ta fitar bayan da shugaba Barack Obama ya zanta da shugabannin kasashen ta wayar talho, ta bayyana cewa dole ne duniya ta dauki dukkanin matakan da suka wajaba domin tunkarar wannan annoba da kawo yanzu ta kashe sama da mutane dubu 4.

A dai bangaren hukumar gudanar da jami’o’in a wasu jihohin kasar Amurka sun soma nuna wa daliban kasashen da ke fama da cutar Ebola wariya, lamarin da kuma ya soma tayar da hankulan wasu daga cikin daliban.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.