Jam’iyyar APC ta lashe zaben Osun
Gwamna mai ci kuma Dan takarar jama’iyyar APC a zaben Jihar Osun Rauf Aregbesola, ya lashe zabe da aka yi jiya Assabar, inda ya sami jimillar kuri’u 394,684 fiye da Dan takarar Jam’iyyar PDP Sanata Iyiola Omisore.
Wallafawa ranar:
‘Yan takarar Gwamna daga Jam’iyyu 20 ne suka fafata a Zaben da aka gudunar a Jihar Osun. Kuma Gwamna Mai ci Aregbesola ya lashe zaben ne a kananan hukumomi 24 daga cikin 30 da ake da su a cikin Jihar.
Dan Takatar Jam’iyyar PDP Iyiola Omisore, shi ne ya zo a matsayi na biyu a zaben da yawan kuri’u 292,750 inda ya samu nasara a kananan hukummoi guda shida.
Fatai Akinbade na Jam’iyyar labour shi ne ya zo a matsayi na uku.
Amma zaben ya fi daukar hankali tsakanin ‘Yan takarar Jam’iyyar APC mai adawa a Tarayya da kuma PDP mai mulki a Najeriya.
Tuni dai shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya mika sakon taya murnarsa ga Aregbesola, akan nasarar da ya samu a zaben.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu