Isa ga babban shafi
Masar

Masar: Kotu ta yanke wa ‘Yan Uwa Musulmi 183 hukuncin kisa

Wata kotu a kasar Masar ta tabbatar da hukuncin kisa akan mambobin Jam’iyyar ‘Yan uwa Musulmi 183 cikinsu har da Shugabansu Mohammed Badie, bayan kotun ta kama su da laifin kisan wasu ‘Yan sanda guda biyu a garin Minya a watan Agusta.

'Yan uwa da dangin magoya bayan hambararren shugaban kasar Masar Mohammed Morsi suna kuka bayan  yanke wa 'yan uwansu da 'yayansu hukuncin Kisa.
'Yan uwa da dangin magoya bayan hambararren shugaban kasar Masar Mohammed Morsi suna kuka bayan yanke wa 'yan uwansu da 'yayansu hukuncin Kisa. REUTERS/Mohamed Abd El Ghany
Talla

Wannan kotun ce a Minya ta yanke wa Mutane 683 hukunci kisa a watan Afrilu, hukuncin da ya janyo suka daga kungiyoyin kare hakkin bil’adama.

A ranar 14 ga watan Agusta ne aka kashe wasu ‘Yan sanda guda biyu a Minya, ranar da kuma ‘Yan sanda suka kashe daruruwan magoya bayan hambararren shugaban kasa Mohammed Morsi a birnin al Kahira.

Tun lokacin da Sojoji suka hambarar da gwamnatin Morsi a watan Yuli, aka kaddamar da farautar mabiya Jam’iyyar ‘Yan uwa Musulmi tare da yanke masu hukuncin kisa.

Kotun ta yanke hukuncin ne a yau Assabar kuma akwai mutane hudu da aka sassautawa hukuncin zuwa daurin rai da rai da suka hada da mata guda biyu. Kotun kuma ta wanke wasu mutane 496, kamar yadda mai gabatar da kara Abdel Rahim Abdel Malik ya tabbatarwa Kamfanin Dillacin Labaran Faransa.

A zaman kotun, an haramtawa ‘Yan Jarida halartar sauraren karar da aka yankewa daruruwan mutanen hukunci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.