Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Shekara daya cur da kifar da gwamnatin Francois Bozize

A kawana a tashi yau 24 ga watan Maris shekara daya kenan da kifar da shugaba Francois Bozize daga karagar mulkin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya.

Tsoffin shugabannin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya Bozize da da Djotodia
Tsoffin shugabannin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya Bozize da da Djotodia AFP PHOTO / STEVE JORDAN
Talla

Kawancen ‘yan tawayen Seleka ne dai ya kori Bozize daga karagar mulki, bayan share tsawon watanni ana fama da yakin basasa a kasar, inda suka daga bisani aka dora Michel Djotodia a matsayin shugaban kasa na riko.

To sai dai sakamakon tashe-tashen hankulan da aka ci gaba da samu a kasar, wannan ya sa shugabannin kasashen yankin Tsakiyar Afrika sun gudanar da taro a birnin Ndjamena na kasar Chadi tare da tilasta masa sauka daga kan mukaminsa.

Saukarsa daga kan wannan mukami ke da wuya sai sabon rikicin ya barke, inda aka samu bayyanar kungiyar ‘yan Anti-balaka wadda ta kunshi kistoci tsintsa, kungiyar da kai hari kan musulmi wadanda take zargi da marawa Djotadia baya. Kasar Faransa da kuma Majalisar Dinkin Duniya sun gargadi kungiyar ta Anti-balaka da ta kawo karshen yadda take kashe musulmi a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.