Lauyoyi sun janye daga taron muhawara a Najeriya
A daidai lokacin da aka kaddamar da taron muhawara domin tattauna batutuwa da dama da suka shafi tarayyar Najeriya, tuni wasu bangarori da ke halartar taron suka bayyana rashin amincewarsu da yadda yake gudana.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Tuni dai kungiyar Lauyoyi ta kasar wato NBA ta sanar da janyewarta daga taron, bisa dalilan cewa ba a ba ta adadin wakilan da ya dace domin su wakilce a wannan taro da take kallo da matukar muhimmanci ba.
Kingiyar dai ta yi zargin cewa akwai wasu kungiyoyi da kuma rukuni na jama’a da aka bai wa kujeru da dama a taron, yayin da su kuma lauyoyi ke da kujera daya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu