Mali
Amirka Ta Soki Tarwatsa Wuraren Ibada a Kasar Mali
Kasar Amirka tayi tir da yadda wasu a kasar Mali sukayi ta tarwatsa wuraren da aka kebe na tarihi a kasar, musamman Masallacin Tinbuktu mai dimbin tarihi da wasu wuraren ibada.Mai Magana da yawun Kasar Victoria Nuland na cewa masu wannan aika-aika su daina nan take.Tun karshen makon daya gabata kungiyar Ansarudeen suka daura dammarar tarwatsa wuraren ibadan dake fadin kasar.
Wallafawa ranar: