Isa ga babban shafi
Faransa-Iran

Hollande ya gana da Rauhani akan Nukiliya

Shugaban Faransa Francois Hollande, ya bukaci a samar da yarjejeniya mai inganci game da shirin Nukiliyar Kasar Iran, yayin da ya bayyana cewa kasar na da ‘yancin mallakar makamashi. Hollande, ya bayyana hakan ne, a wata tattaunawa da ya yi da Shugaban Kasar Iran Hassan Rouhani.

Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani
Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani
Talla

Hollande ya jajirce cewa, Iran na da ‘yancin amfani da Nukiliya ta bangaren makamashi, lamarin da ya sa ya dage kan cewa, ya kamata a gaggauta cim ma yarjejeniya mai daurewa da kasar.

Ganawa tsakanin Holland da Rouhani, na zuwa ne, a daidai loakcin da aka dawo domin shiga zagayen karshe na tattaunawa tsakanin Iran da manayan kasashen duniya a kasar Switzerland, inda ake fatan cim ma yarjrjeniya.

Shugaban Kasar Iran, ya zanta da Firaministan Birtaniya David Cameron, ta wayar Tarho, inda ya bayyana ma sa cewa, Kasarsa na bukatar a cire ma ta dukkanin takunkuman da aka kakaba ma ta.

Tun a shekara ta 2013 ne, manyan kasashen duniya 6, da ke tattaunawa da Iran, suka bukaci ta yi watsi da wannan shiri da ake zargin cewa tana kokarin kera makaman nukiliya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.