Isa ga babban shafi
Faransa

An gano inda Jirgin Jamus ya fado

Kwararru tare da taimakon jami’an tsaro sun soma  bincike a wurare da jirgin saman   na kamfani Germanwings ya fadi a wani  yankin kasar Faransa.

Shugabannin Kasashen Jamus, Faransa da Spain, a ziyarar da suka kai a yankin hadarin
Shugabannin Kasashen Jamus, Faransa da Spain, a ziyarar da suka kai a yankin hadarin
Talla

Hadarin dai da ya yi sanadiyyar mutuwar  mutane 150 da ke cikin jirgin da suka hada da Fasinjoji 144 da Ma'aikatan jirgin 6.

Shugaban kamfanin Jirage na Lufthansa, Carsten Spohr, ya bayyana cewa jirgin bashi da wata masala.

Kafin aukuwar hatsari jirgin  ya kwashe tsawon shekaru 25 yana aiki.
 

Shugabannin kasashen Faransa, Jamus da kuma Spain, sun kai ziyara a kusa da inda lamarin ya faru, inda suka nuna alhinin  su dangane da wannan hatsari da ake kallo a matsayin daya daga cikin mafi muni da ya faru a nahiyar Turai.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.