Isa ga babban shafi
Faransa

‘Yan Jaridu 66 aka yi wa kisan gilla a 2014

Kungiyar da ke sa ido kan ayyukan ‘Yan Jarida wato Reporters Without Borders tace ‘yan Jaridu 66 aka yi wa kisan gilla a cikin watanni 12 da suka gabata. A cikin rahotan da kungiyar ta gabatar ta bayyana fille kan Jamse Foley da Steven Sotloff da mayakan IS suka yi a Iraqi a matsayin irin hadarin da ke tattare da aikin dauko rahoto a inda ake samun tashin hankali.

Hoton Bidiyon da Mayakan IS suka hallaka Dan Jarida  James Foley
Hoton Bidiyon da Mayakan IS suka hallaka Dan Jarida James Foley Reuters
Talla

Kungiyar tace yadda aka kashe wadannan ‘yan Jaridu biyu ya sabon abu ne aka saba gani a duniya.

Kungiyar ta kuma bayyana cewar an yi garkuwa da ‘Yan Jarida 119. 33 a Ukraine, 29 a Libya da kuma 27 a Syria.

Kungiyar tace jimillar ‘Yan Jarida 720 aka kashe tun 2005 zuwa yanzu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.