Isa ga babban shafi
OMS/WHO

Yawan mutanen dake kamuwa da annobar cutar Ebola zai karu da mutane dubu 10 a kowane mako inji WHO

Hukumar lafiya ta duniya ta yi gargadin cewa abu ne mai yiyuwa, yawan mutanen da ke kamuwa da cutar Ebola ya zarta dubu 10 a kowane mako matukar dai kasashen duniya ba su dauki matakan da suka wajaba ba, domin tunkarar wannan annoba ba.

Talla

Har ila yau hukumar lafiyar ta bayyana cewa yawan mutanen da ke mutuwa sakamakon kamuwa da cutar Ebola sun kai kashi 70 cikin dari a kasashen 3 da cutar ta bulla a cikinsu dake yankin yammacin Afrika, kamar yadda Bruce Aylward, mataimakin darakatan hukumar lafiya ta Majalisar DD Ya sanar a jiya talata

Yanzu haka dai za a iya cewa cutar ta Ebola ta kusa zama annobar daukacin kasashen duniya sakamakon mutuwar wani jami’in Majalisar DD da ya kamu da cutar, bayan kwantar da shi a wani asibiti dake kasar Jamus a jiya talata, yan sa’oi bayan soma gudanar da zaman taron kwamitin tsaro na MDD, kan yaki da cutar ta Ebola, wace ta yi sanadiyar mutuwar sama da mutane dubu 4 a yankin yammacin Afrika

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.