Isa ga babban shafi
Faransa-Syria

Faransa ta ba ‘Yan tawayen Syria makamai

Faransa ta bai wa ‘yan tawayen kasar Syria makamai, domin tunkarar dakarun gwamnatin shugaba bashar Al Assad, da kuma mayakan jahadin da suka mamaye wasu yankuna a kasashen Iraqi da Syria.

Shugaban Faransa, François Hollande
Shugaban Faransa, François Hollande REUTERS/Benoit Tessier
Talla

Shugaba Francois Hollande ya shaidawa manema labarai cewa sun aikawa ‘Yan tawayen da Makamai a watannin da suka gabata.

Shugaban yace matakin ya zama dole domin taimakawa mutanen Syria da ke son tabbatar da mulkin demokuradiya a kasar.

A cikin wata tattaunawa da Jaridar Le Monde, Hollande yace Faransa ta yi wa ‘Yan tawayen Syria guzurin makamai a bisa sharrudan muradun Turai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.