Syria-Amurka-Birtaniya - 
Wallafa labari : Talata 07 Feberairu 2012 - Bugawa ta karshe : Talata 07 Feberairu 2012

Amurka da Birtaniya sun janye jekadunsu daga syria

Wasu masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Assad sun yi da'ira a ofishin kedancin kasar Syria a Tunisia
Wasu masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Assad sun yi da'ira a ofishin kedancin kasar Syria a Tunisia
Reuters / Zoubeir Souissi

Daga Awwal Ahmad Janyau / Garba Aliyu

Kasar Amurka da Birtaniya sun janye jakadunsu daga kasar Syria saboda fargabar tsaro da rashin amincewa da yadda ake ci gaba da murkushe masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Bashar al Assad.

Birtaniya ta janye jakadanta amma Amurka ta rufe ofishin jekadancinta al’amarin da Obama ya bayyana cewa ya sha banban da rikicin kasar libya inda kasashen yammaci suka shiga tsakani wajen kawo karshen Kanal Gaddafi.

Sakataren harakokin wajen Birtaniya Williams Hague yace sun gayyaci Jakadan kasar ne na Birtania domin nuna rashin amincewar kasar game da yadda lamurra ke gudan a kasar Syria.

A cewar Williams Hague yanzu Birtaniya zata tura wasu sabbin matakan karya kasar Syria, tare da neman Majalisar Dinkin Duniya daukar matakan daya dace domin kawo karshen zubar da jini da ake samu a cikin kasar

Shugaban Amurka Barack Obama yace suna bin abubuwansu ne bisa tsarin diflomaciya.

Bayanai daga kasar ta Syria na nuna cewa a ajiya rayukan mutane akalla 48 aka rasa, sakamakon ruwan rokoki da jami’an tsaron Gwamnati suka yi ta aikewa akan Jama’a a birnin Homs.

 

tags: Amurka - Barack Obama - Bashar al Assad - David Cameron - Ingila - Syria
KAN MAUDU'I GUDA
Ra'ayoyi
Bada ra'ayi kan wannan magana
The content of this field is kept private and will not be shown publicly.
To prevent automated spam submissions leave this field empty.
CAPTCHA
This question is for testing whether you are a human visitor and to prevent automated spam submissions.
Image CAPTCHA
Enter the characters (without spaces) shown in the image.
Close