Duniya

Syndicate contentDUNIYA
Ratko Mladic a zauren kotun duniya lokacin sauraren karar shi a ranar 3 Yuni 2011.
16/05/2012 - Serbia-ICC

Sauraren karar Kwamandan Serbia, Ratko Mladic a gaban kotu

Tsohon kwamandan Serbia, Janar Ratko Mladic, ya gurfana a gaban kotun Duniya a birnin Hague domin fuskantar zargi 11 na laifukan yaki da kisan kare dangi da keta hakkin bil’adama a yakin Bosnia a shekarar 1992-95.

Luis Moreno-Ocampo,Mai gabatar kara a kotun hukunta manyan laifuka ta ICC
15/05/2012 - ICC-Congo

ICC ta bukaci sabon sammaci ga shugaban ‘Yan tawayen Congo

Mai Gabatar da kara na kotun hukunta manyan laifufuka, Luis Moreno Ocampo, ya nemi wani sabon sammacin kama shugaban ‘Yan Tawayen Congo, Janar Bosco Ntaganda, da Sylvester Mudacumura, wadanda suka jagoranci tawayen da aka kashe miliyoyin mutane a cikin shekaru 20 da suka gabata.

Wani yana neman tsira da ranshi a wani hari da aka kai a Libya
14/05/2012 - Libya-NATO-HRW

NATO ta kashe fararen hula 72 a Libya, inji HRW

A wani Rahoton da Hukumar kare hakkin Dan adam ta Human Rights Watch ta fitar, rahoton yace a bara wani hari da kungiyar NATO ta kai ta sama ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 72 a Libya, tare da zargin kawance kasashen Turai da suka kaddamar da yakin kawar da Gaddafi.

François Hollande, tare da shugaban kungiyar tarayyar turai  Herman Van Rompuy
11/05/2012 - Amurka-Faransa-Diflomasiya

Wasu manzannin A mruka 3 sun ziyarci sabon shugaban kasar Fransa a yau juma'a

Wasu manzannin diplomasiyar kasar Amruka guda 3 a yau juma’a sun gana da shugaban kasar Framsa mai jiran garo Francois Hollande a birnin Paris, kafin ziyarar da yake shirin kaiwa a kasar Amruka a moko mai zuwa, inda sabon shugaban na Fransa zai gana da shugaban kasar Amruka Barak Obama.

Magungunan cutar HIV/AIDS
11/05/2012 - Amurka

Ana shawarar fara amfani da maganin rigakafin HIV

MASU kula da lafiya a kasar Amurka suna shawara kan yuwuwar fara amfani da wani magani mai suna Truvada, a matsayin wanda za a yi amfani da shi don rigakafin cutar HIV, maimakon bayar da shi don warkar da wadanda suka kamu da cutar AIDS.

Shugaban kasar Amurka Barack Obama
10/05/2012 - Amurka

Obama ya yi na’am da auren jinsi a Amurka

Shugaban Kasar Amurka, Barack Obama ya fito karara inda ya bayyana goyan bayan shi ga auren jinsi guda, a dai dai lokacin da Jahar North Carolina ta zama Jiha ta 30 da taki amincewa da auren.

Ranar Mata ta duniya
10/05/2012 - Tattaunawa

Ranar Mata ta duniya

A yau alhamis 10 ga watan Mai,  rana ce  da majalisar dinkin duniya ta ware domin ta zama ranar Mata ta duniya, inda mata kan bayyana halin da suke ciki na matsi ko dadi, tare da ...

Kofi Annan a lokacin da yake jawabi a zauren Majalisar Dinkin Duniya game da Syria.
09/05/2012 - Syria-MDD

Annan yace tsarinsa na zaman Lafiya a Syria shi ne mataki na karshe

Jekadan Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Syria, Kofi Annan, ya shaidawa kwamitin Sulhu cewa, shirinsa na neman zaman lafiya shi ne mataki na karshe don kaucewa yakin basasa a kasar, a yayin da dakarun gwamati ke ci gaba da diran mikiya kan masu zanga zanga, da azabtar da fursunoni.

Shugaban Amurka Barack Obama a yakin neman zaben shi Viginia
08/05/2012 - Amurka-Faransa

Rikicin Duniya: Sarkozy ya bi sahun Berlusconi, ko Obama zai kai labari?

A ranar 6 ga watan Mayu ne Nicolas Sarkozy daya daga cikin aminan Shugaban kasar Amurka Barack Obama ya sha kaye a zaben Shugaban kasa bayan Faransawa sun juya masa baya inda suka zabi dan ...

Matan kasar Afghanistan a lokacin gudanar da bukin ranar mata a yankin Ghazni a ranar 8 ga watan Maris
08/05/2012 - Lafiya

Kasar Norway ne iyaye mata suka fi shan dadi amma a Nijar suka fi shan wahala

A wani sabon Rahoto game da halin rayuwar iyaye mata da hukumar kare lafiyar kananan yara ta fitar, ya nuna Nijar ce kasar da iyaye Mata ke shan wahala bayan maye gurbin kasar Afghanistan a karon farko. Kasar Norway ce a matsayin kasa ta farko da iyaye Mata ke shan dadi a jerin kasashe 165 da aka kwatanta rayuwarsu.

François Hollande Sabon shugaban kasar Faransa wanda ya kada Nicolas Sarkozy
07/05/2012 - Zaben Faransa

Shugabannin kasashen duniya sun taya Hollande Murnar lashe zaben Faransa

Shugabannin kasashen duniya da na Turai sun mika sakon taya murna ga Francois Hollande wanda ya lashe zaben shugaban kasar Faransa bayan ya kada Nicolas Sarkozy a zagaye na biyu da aka gudanar a ranar 6 ga watan Mayu.

Jaridun kasashen Duniya game da shan kayen Nicolas Sarkozy.
07/05/2012 - Zaben Faransa

Sharhin Jaridun duniya akan nasarar Hollande a Faransa

Hankalin jaridun kasashen Duniya baki daya ya karkata ne akan nasarar da Francois Hollande ya samu a zaben Faransa bayan kayar da Nicolas Sarkozy.

Chen Guangcheng tare da Jekdadan Amurka a China Gary Locke
04/05/2012 - China-Amurka

China tace Chen zai iya neman izinin karatu a kasashen Waje

Gwamnatin kasar China tace Makaho dan rajin kare hakkin Bil’adama, Chen Guangcheng, zai iya neman izinin karatu a kasashen waje, a wani mataki na bude kofar kawo karshen sabanin da aka samu bayan ya tsere zuwa Ofishin jekadancin Amurka.

Les manchettes des journaux ivoiriens commémorent ce 11 avril 2012, à leur manière,  l'arrestation de Laurent Gbagbo, il y a un an jour pour jour.
03/05/2012 - Sharhin Jaridu

Sharhin jaridun duniya

PRESS REVIEW 03-05-012

Chen Gaucheng Wata maikaciyar Asibiti na dauke da shi saman kujera.
03/05/2012 - China-Amurka

Hu Jintao ya nemi mutunta Juna tsakanin Amurka da China

Shugaban Kasar China, Hu Jintao, ya bukaci Amurka da China mutunta mutuncin juna, sakamakon matsalar da aka samu na boye makaho mai kare hakkin Bil Adama, Chen Guangcheng, a Ofishin Jakadancin Amurka.

wasu matasan daga sozojin kasar rasha
02/05/2012 - Rasha

Sozojin Rasha biyar sun rasa rayukansu a cikin wani hadarin fashewar Nakiya a yau.

Sojan kasar Russia 5 ne suka gamu da ajalinsu a yau laraba sakamakon tarwatsewar nakiya, a wani wuri da Sojan kasar ke koyon harbi, a tsakiyar kasar

Marigayi Osama Bin Laden Shugaban kungiyar al-Qaeda da wanda ya gaje shi Aymar Zawahiri
02/05/2012 - Pakistan-Amurka-Afghanistan

An cika shekara da kisan Osama, Obama ya yi kiran sansatawa da Taliban

A rana irin ta yau ce dakarun Amurka suka ce sun kashe Osama bin Laden a Pakistan, amma kuma shugaban Amurka Barrack Obama ya yi kiran zama teburin sasantawa da Taliban a wata ziyarar bazata da ya ...

France 24 journalist Roméo Langlois
01/05/2012 - Colombia-France-journaliste-FARC

Alamu na nuna cewa, kungiyar yan awaren FARC a kasar Colombia ce, ta sace dan jaridar nan na tashar TV din France24.

Romeo Langlois, dan jaridar nan dan kasar Fransa na rike ne ga hannun kungiyar yan awaren FARC a kasar ta Colombia.

Wani Allo dauke da zanen Nicolas Sarkozy da Jam'iyyarsa a lokacin da ma'aikata suka fito zanga-zanga a birnin Lyon na Faransa
01/05/2012 - Duniya

Ranar Ma’aikata: zanga zanga ta barke a wasu kasashen duniya

Kungiyoyin kwadago a kasashen Turai sun shirya gudanar da zanga-zangar adawa da matakan tsuke bakin aljuhun gwamnati domin gudanar da hutunsu na ma’aikata. Ma’aikata a Spain sun shiga zangar zangar ne saboda matsalar rashin aikin yi.

a yau ne aka gudanar da shagulgulan ranar ma'aikata ta duniya, ga wasu ra'ayoyin masu saurarenmu kan wannan rana.
01/05/2012 - Tattaunawa

a yau ne aka gudanar da shagulgulan ranar ma'aikata ta duniya, ga wasu ra'ayoyin masu saurarenmu kan wannan rana.

A YAU talata 1ga watan Mayu 2012 rana ce da Majalisar dinkin duniya ta kebe domin ma'aikatan kwadago a duniya, inda suke yin amfani da damar wajen bayyanawa mahukumtan kasashensu matsalolin da ...

Close