Isa ga babban shafi
Afghanistan

Afghanistan za ta gana da Taliban a Qatar

Wakilan gwamanatin kasar Afghanistan sun halarci kasar Qatar, inda za su tattauna har na tsawon kwanaki biyu da wakilan kungiyar Taliban  

Mayakan Taliban
Mayakan Taliban AFP PHOTO / Noorullah Shirzada
Talla

Tattaunawar za ta gudana ne da nufin kawo karshen yakin Kasar da aka shafe tsawon loakci ana tafkawa.

Har ila yau, ganawar za ta samu halartar wakilai daga Kasar Pakistan kamar yadda mataimakin shugaban kwamitin samar da zaman lafiya ta Afghanistan, Abdul Hakim Mujahid ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa na AFP.

Tun a shekara ta 2010 ne, tsohon shugaban Afghanistan, Hamid Karzai ya samar da kwamitin domin tattaunawa da kungiyar Taliban da sauran kungiyoyin dake tada kayar baya a Kasar, sai dai har yanzu ba a samu cikakkiyar nasara ba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.