Saudi
Kasashen Larabawa za su kafa runduna don yakar ta’addanci
Ministocin Kasashen waje na kungiyar kasashen Larabawa sun amince da shirin kafa rundunar soji da za ta yaki ‘yan ta’addan da ke yin barazana a yankin. Ministan harkokin wajen Masar Sameh Shoukry yace zasu mika Kudirin da ministocin suka amince da shi ga shugabanin kasashen Larabawa a taron da zasu gudanar a karshen mako.
Wallafawa ranar:
Talla
Matakin na zuwa ne bayan Saudi Arabiya ta kaddamar da hare hare kan ‘Yan tawayen Yemen tare da neman taimakon sauran kasashen da ke Yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu