Syria
ISIS ta tilastawa 'Yara 400 daukan makamai
Wata kungiya mai cibiya a Birtaniya dake sa’ ido a kan Syria, ta bayyana cewa akalla kananan Yara 400 kungiyar ISIS ta tilastawa daukar makamai
Wallafawa ranar:
Talla
Shugaban kungiyar Rami Abdulrahman ya ce mayakan na kwashe yara ne da basu haura shekaru 18 ba, daga makarantu, masallatai da kuma Garuruwa da mayakan ke kai hari
Rami ya kuma kara da cewa yaron da aka haska a sabon fai-fai bidiyo da mayakan suka aiko, wanda ya harbe wani dan kasar isra’ila, na daga cikin iri-irin yaran da kungiyar ke dauka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu