Yemen
'Yan Kunar Bakin Wake Sun Kashe Mutane 142 a Masallacin Yemen
A kasar Yemen wani dan kunar bakin wake y kai hari cikin wani masallacin Juma’a a Sanaa yau inda ya kashe mutane 142.Wannan na daga cikin munanan hare hare a kasar dan tsakanin nan.Harin na yau na zuwa ne kwana daya bayan gwabza fada tsakanin dakaru masu goyon bayan Shugaba Abedrabbo Mansour Hadi da kuma mayakan Huthi a garin Aden dake karbar bakuncin akasarin jamian Gwamnati da jakadun kasashen waje.‘Yan kunar bakin wake na yau sun hari masallatai biyu ne dake Sanaa babban birnin kasar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: