Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falesdinawa

“Goyon bayan Falasdinawa illa ne ga Isra’ila”

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi koken cewar goyan bayan da kasashen Turai ke bai wa Falasdinawa kan shirin Majalisar dinkin Duniya na tilasta ma ta ficewa daga yankunan da ta ke mamaye da su illa ne ga Isra’ila. Netanyahu yace duk wani yunkuri makamancin haka zai haifar da tabarbarewar al’amura a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma Isra’ila, saboda haka ba za su amince da shi ba.

Sakataren harakokin wajen Amurka John Kerry yana tabewa da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a wata ganawa da suka yi a birnin Kudus
Sakataren harakokin wajen Amurka John Kerry yana tabewa da Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a wata ganawa da suka yi a birnin Kudus Reuters/Jason Reed
Talla

Birtaniya da Sweden da Faransa da Spain sun amince a ba Falasdinawa 'Yanci. Amma Isra’ila ta yi watsi da matakin tana mai cewa zai kara lalata yunkurin komawa teburin tattaunawar sasanta rikicin gabas ta tsakiya.

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ce Netanyahu da John Kerry sun yi wata duguwar ganawa kan tsaron kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.