Dubban Kurdawa sun bar gidajensu a kasar Syria
Majalisar Dinkin Duniya ta ce a cikin sa’o’I 24 da suka gabata, Kurdawan Syria akalla dubu 70 ne suka bar gidajensu sakamakon barazanar da suke fuskanta daga mayakan jihadi na kasar.
Wallafawa ranar:
Yanzu haka dai daruruwan dakarun kungiyar ta mayakan jihadi ne suka yi wa garin Ain Al-Arab wanda mafi yawan mazaunansa Kurdawa ne kawanya, yayin da a hannu daya ake ci gaba da gwabza fada tsakanin masu da’awar jihadin da kuma mayakan sa-kai na kurdawa.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce akwai bukatar daukar matakan gaggawa domin bai wa fararen hular yankin kariya daga mayakan wannan kungiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu