Isra'ila-Syria
An harba makaman roka daga Syria zuwa Golan
Yayin da aka shiga rana ta 48, a yakin da ake yi tsakanin Isra’ila da kungiyar palasdinawa ta Hamas, yau Lahadi wasu makaman rokan da aka harba daga kasar Syria, sun fada a yankunan tiddan Golan, da Isra’ila ta mamaye. Mai magana da yawun rundunar sojan kasar ta Yauhudu tace, a kalla makaman roka 5 ne suka sauka a wurare daban daban a tiddan na Golan, sai dai sojojin basu mayar da martani ba.Ko a cikin watan daya gabata, wasu makaman rokan da aka harba kasar Isra’ila daga Syria, sun janyo martani kan wuraren da ke hannun sojan na Syria.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: