A ranar 18 ga watan Disemba ne aka fara kaddamar da zanga-zangar adawa da gwamnatocin kasashen Larabawa har zuwa yanzu. Domin neman girka gwamnatin Demokradiyya a kasashen Tunisia da Masar da Libya da Syria da Bahrain da Yemen da sauran kasashen Larabawa bayan kwashe tsawon shekaru shugabannin kasashen na gudanar da mulki sabanin na Demokradiyya.
An fara Zanga-zangar ne a kasar Tunisia inda ta yi sanadiyar hambarar da gwamnatin Zainul Abidina bn Ali, daga nan kuma zanga-zangar ta bazu zuwa kasar Masar da Libya inda ta yi sanadiyar kawo karshen mulkin Hosni Mubarak na Masar da Kanal Ghaddafi na Libya.
Mutane da dama sun rasa ransu saniyar zanga-zangar. A kasar Syria akalla sama da mutane 5,000 ne aka kashe, inda a kasar Libya fararen hula da dama suka mutu bayan shiga tsakanin kungiyar NATO domin taimakawa ‘Yan Tawaye.
Ana ci gaba da Zanga-zanga kuma ana dakun Sakamakon zabe |
|
|
|
|
Rikicin kasar Syria |
|
|
Rikicin kasar Syria |
|
|
Sabuwar gwamnatin Tunisia |
|
|
Rikicin kasar Syria |
|
|
Zanga-zangar Dandalin Tahrir |
|
|












