Falesdinawa 1,500 da ke yajin cin abinci a gidan yarin Isra’ila, sun kawo karshen fafutukarsu, bayan kwashe sama da watanni biyu, saboda wata yarjejeniyar da aka kulla tsakanin Isra’ila da Falasdinu.
A yau juma’a kasar Pakistan ta bayyana cewa a ranar 11 zuwa 12 ga watan yunin gobe ne, za a koma wata sabuwar tattaunawa tsakaninta da kasar Indiya dangane da tsaunukan Siachen, dake dankare ...
A kasar Indonesia, a yau juma’a masu aikin ceto, dauke da jikkunan zuba gawarwaki sun fara isa zuwa tsaunin nan da jirgin saman kasar Rasha, dauke da mutane 45 ya fadi.
Mahukumtan kasar Iraki sun bayyana cewa, a yau Alhamis sun gano gawwakin wasu mutane 7 da aka kashe ta hanyar harbin Bindiga a kai, bayan da aka daure masu hannuwa da idanu, a rairayin saharar yankin tsakkiyar kasar.
Akalla mutane 55 ne aka kashe a yayin da wasu sama da 372 suka jikkata a yau alhamis, sakamakon wasu hare-haren ta’addanci da aka kai da bam a birnin Damas babban birnin kasar Suriya, kamar yadda ministan cikin gidan kasar ya bayyana a wata sanarwa ta tashar talabijin din gwamnatin kasar.
Hukumar ‘Yan Sanda ta Duniya ta fitar da sanarwar bada umurnin Cafke Mataimakin Fira ministan Iraqi Tareq al-Hashemi wanda bisa zargin shi da taimakawa da bada tallafin kudi ga ayyukan ta’adanci.
A kokarin shi na kawo karshen tashe tashen hankulan da ke faruwa a kasar Bahrain, Sarki Hamad ya amince da gyaran da aka yi wa tsarin mulkin kasar amma ‘Yan adawa sun nuna rashin amincewar su da karfin da aka kara wa majalisar kasar, inda suka ce bai isa ba.
Wasu palastinawa 2 da kasar Izra’ila ke tsare da su, wadanda ke yajin kin cin abinci yau da kwanaki 65 da suka gabata, a yau alhamis sun bayyana a gaban madaukakiyar kotun kasar, wace ta sake duba bukatar da suka gabatar na neman a sake su, kamar yadda lauyan kungioyar kare hakkin dan adam ta palastinawa ya sanar a yau.
Jagorar yan adawar kasar Myanmar Uwargida Aung San Suu Kyi a yau ta yi rantsuwar kama aiki a matsayin wakiliyar Majalisar kasar, alamarin daya bude sabon babi a siyasar kasar.
Akalla sama da mutane 10 ne aka kashe a yayinda wasu da dama suka jikkata a cikin wata taho mugamar da ta hada yan adawa da magoya bayan sozojin dake mulki, a kusa da ofishin ma’aikatar ministan tsaron kasar Masar
A kasar India wani kwale-kwale dauke da mutane akalla 250 ya nutse a wani kogi, bayan wani mummunar iskar da ya taso, amma anyi katarin ceto mutane akalla 50.
A yau litanin wasu hare-hare sun yi sanadiyar mutuwar mutane da dama mafiya yawansu kuma dakarun tsaron kasar Syriya a garin Ibleb dake yankin arewa maso yammacin kasar, kwana guda bayan isar janar Robet Mood shugaban tawagar masu zura ido MDD kan yarjejeniyar tsagaita buda wuta, a kasar ta Syriya inda tashe tashen hankulla suka yi sanadiyar mutuwar mutane 70 a wannan mako.
Dan gwagwarmayar kare hakkin dan adam din nan Chen Guangcheng da yayi nasarar tserewa daga gidansa inda mahukumtan China ke tsare da shi, yanzu haka ya na ofishin jakadancin kasar Amruka a birnin Pekin babban birnin kasar ta China, kamar yadda dan gwagwarmayar nan Hu Jian ya sanar, sai dai kuma ya ce bai nemi mafakar siyasa ba.
A tashe tashen hankullan da ke wakana a kasar Iraki, a yau litanin mutane 6 ne aka kashe a birnin Bagadad babban birnin kasar Iraki, mutanen da suka hada da wata uwa da yaranta 3, da aka kashe a gidansu ta hanyar daddaba masu wuka, kamar yadda majiyoyi masu kama da juna suka tabbatar.
Gwamnatin Pakistan ta kori iyalan marigayi Osama bin Laden zuwa Saudiyya da suka kunshi ‘Yayansa da matansa uku. Iyalan Osama sun kwashe lokaci suna zaune a Pakistan tun bayan da dakarun Amurka suka kashe shi a watan Mayun bara.
‘Yan rajin tabbatar da Demokradiya a Syria sun ce Akalla mutane 70 suka mutu sanadiyar wani hari da aka kai a birnin Hama. Sun ce gidaje da dama ne suka kone musamman a yankin Mashaa at-tayyar bayan fashewar bama bamai.
Dakarun sojan kasar Yamen sun bayyana daukar sabin dubaru a yakin da suke yi da dakarun kungiyar Alka’ida tun farkon watan mayun 2011 da ta gabata a garin Zinjibar dake yankin kudancin kasar ta Yamen.