Mali
An kashe wani Soja dake aiki da MDD a Mali
Wasu mutane dauke da makamai sun bude wuta a kan dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD a birnin Bamako na kasar Mali, inda suka kashe soja daya sannan suka raunata wani.
Wallafawa ranar:
Talla
Lamarin dai ya faru ne a cikin daren jiya litinin lokacin da dakarun na MDD ke gudanar da sintiri a birnin Bamako, rahotanni sun ce sojojin da aka harba ‘yan kasar Bangladesh ne.
Har yanzu ba a tantance ‘Yan bindigar ba wadanda suka bude wa Dakarun wuta ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu