Isa ga babban shafi
Burundi

‘Yan Burundi na fama da Kwalera a Tanzania

Majalisar Dinkin Duniya tace kimanin mutanen kasar Burundi 3,000 ke fama da cutar Kwalera a sansaninsu na ‘Yan gudun hijira a Tanzania bayan sun tallaka kasar saboda rikici. Mahukuntan lafiya a Tanzania sun ce akalla mutane 33 suka mutu tun barkewar cutar a kauyukan Kogunga da Nyarugusu.

Sansanin da ake kula da lafiyar 'yan gudun hijirar kasar Burundi a Tanzania
Sansanin da ake kula da lafiyar 'yan gudun hijirar kasar Burundi a Tanzania REUTERS/Thomas Mukoya
Talla

Hukumar kula da ‘Yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya tace adadin na iya zarce haka, domin kimanin mutane 300 zuwa 400 ke kamuwa da cutar a kullum.

Majalisar Dinkin Duniya tace sama da ‘yan Burundi 100,000 suka fice kasar zuwa makwabta bayan barkewar zanga-zangar adawa da matakin shugaba Nkurunziza na neman wa’adin shugabanci na uku.

Hukumar ‘Yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya tace mutanen Burundi 70,200 suka tsere zuwa Tanzania, 26,300 suka tsallaka zuwa Rwanda, yayin da 10,000 suka shiga kudancin Kivu a kasar Jamhuriyyar Congo.

Yanzu haka 'Yan sanda na ci gaba da arangama da masu zanga-zanga a Burundi, lamarin da ke haifar da fargaba ga al'ummar kasar na yiyuwar barkewar yakin basasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.