Isa ga babban shafi
Najeriya

An yi watsi da tuhumar kisa da ake yi wa Wasila

Masu gabatar da kara a Najeriya sun yi watsi da tuhumar kisa da ake yi wa Wasila Tasi’u ‘yar shekaru 15 kan zargin ta kashe Mijinta ta hanyar sa masa guba a abinci. Babban mai gabatar da kara Lamido Abba ya bukaci Kotun Gezawa a Kano ta yi watsi da shari’ar.

Kotun Gezawa inda ake shari'ar Wasila da ake zargi ta kashe mijinta
Kotun Gezawa inda ake shari'ar Wasila da ake zargi ta kashe mijinta Dailymail
Talla

Wasila mai shekaru 14 a lokacin da aka daura mata aure da Malam Umar Sani, na kokarin kaucewa hukuncin kisa akan zargin ta kashe mijinta mai shekaru 35 da hanyar sa masa guba a Abinci.

Amma masu gabatar da kara na ganin Wasila da ta fito daga gidan Talakawa ta saka wa Mijinta guba ne saboda auren dole.

Al’amarin dai ya janyo mutuwar wasu mutane uku wadanda suka ci abincin da Wasila ta sanya wa Guba bayan an kammala bikinsu da Malam Umar.

Yanzu haka kotun ta dage shari'ar har zuwa 9 ga watan Yuni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.