Ana ci gaba da zanga zanga a Burundi duk da hukuncin kotu
A Kasar Burundi, mutane na ci gaba da zanga-zangar adawa da matakan zarcewa da mulki na Shugaba Pierre Nkurunziza, bayan da Kotun Kula da tsarin mulki ta wanke shi domin zarcewa da mulki wa’adi na uku
Wallafawa ranar:
Duk da cewar mataimakin shugaban kotun tsarin mulkin, yaki sanya hannu cikin shawarar da kotun ta yanke, kuma ya tsere ya bar kasar, wannan bai hana gabatar da matsayin kotun ba, da sauran alkalanta shida suka tsaida.
Masu bore dai sun ce, basu amince ba, kuma yanzu suka fara zanga-zangar nuna kyamar matakin.
Ta bangaren Gwamnatin dai, ta ce idan har sun jingine bore to kuwa za a sako wadanda ake tsare da su saboda shiga boren da aka kwashe sama da mako daya ana yi.
Kawo yanzu boren yayi sanadiyar mutuwar mutane akalla 13. Kuma mutane da dama sun jikkata, yayinda bayanai ke cewar jamian tsaro na tsare da mutane kusan 600.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu