Isa ga babban shafi
Najeriya

Buhari na kan gaba a zaben Najeriya

Dan takarar Shugaban kasa Janar Muhammadu Buhari na Jam’iyyar APC mai adawa ne a kan gaba a sakamakon zaben shugaban kasa na Jihohi 18 da Abuja da hukumar zaben Najeriya ta sanar, inda ya ba shugaba Goodluck Jonathan tazarar kuri’u sama da Miliyan biyu.

Magoya bayan Janar Muhammadu Buhari na Jam'iyyar APC a Najeriya
Magoya bayan Janar Muhammadu Buhari na Jam'iyyar APC a Najeriya REUTERS
Talla

Buhari na Jam’iyyar APC ya lashe Jihohi 10, yayin da Jonathan na PDP ya lashe 8 hadi da birnin Tarayya Abuja, a sakamakon da hukumar zaben kasar ta sanar na Jihohi 18.

Sai da misalin karfe 10 na safiyar Talata ne za a ci gaba da bayyana sakamakon zaben a sauran Jihohi 18.

Zuwa yanzu Buhari ya samu kuri’u Miliyan 8.5, tazarar kuri’a Miliyan biyu tsakanin shi da Jonathan. Amma cikin manyan Jihohin da ba a bayyana ba akwai Lagos da Jihar Rivers masu yawan kuri’u.

Reuters

Buhari ya samu Kuri’u da yawa a Jihohin Kano da Katsina da Kaduna da Jigawa da Oyo da Kwara da Kogi da Ondo da Osun da Ogun.

Jonathan ya samu Kuri’u a Jihohin Ekiti da Enugu da Nasarawa da Abia da Imo da Abuja da Akwa Ibom da Filato da Anambra.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.