Mayakan Boko Haram sun far wa kauyukan jihar Borno
Mayakan kungiyar Boko Haram sun kai samame a wasu kauyukan da keda iyaka da kasar Kamaru a yankin arewa maso gabashin Nigeria, bayan da sojojin kasar Chadi suka musu luguden wuta a wuraren da suka boye. Rahotannin dake fitowa daga yankin na cewa mayakan, dauke da manyan makamai sun kai munanan hare hare a kan kauyukan dake yankin Kalan-Balgea jihar Borno, inda suka yi ta harbi, tare da daddatsa mutanbe da adda.Wani mazaunin yankin yace maharan suna far wa kauyukan ‘yan Shuwa ne, da suke kabila daya da akasarin sojojin na Chadi.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: