Isa ga babban shafi
Cote d'Ivoire

Matar Gbagbo ta yi watsi da tuhumar da ake ma ta

Matar Tsohon shugaban kasar Cote d’Ivoire Simone Gbagbo ta ki amincewa da tuhumar da ake ma ta na taimakawa wajen tashin hankalin siyasar da aka samu a kasar a lokacin da mijinta ya ki sauka daga mulki bayan an kada shi a zabe. Kasar Cote d’Ivoire ta ki mika matar tsohon shugaban kasar ga kotun duniya da ke neman ta ruwa ajallo inda ta amince a yi ma ta shari’a a gida.

Simone Gbagbo
Simone Gbagbo AFP PHOTO / SIA KAMBOU
Talla

Ana tuhumar Simone da hannu wajen tashin hankalin da ya yi sanadiyar kashe mutane 3,000 da ke adawa da mijinta Laurent Gbagbo wanda yanzu haka ya ke tsare a hannu kotun duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.