Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Dubban Mutane sun kauracewa gidajensu a Afrika ta Tsakiya

Dubban mutane ne, suka kauracewa gidajensu a ‘yan kwanakinnan, sakamakon tarzomar da ke cigaba da tsananta a jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta sanar kenan. 

'yan gudun Hijira.
'yan gudun Hijira. Reuters
Talla

Jama’ar sun kauracewa gidajensu ne, dan tsoron salwantan rayukansu sakamakon farmakin ‘yan tawaye da kuma ke yiwa mata fyade bayaga fashin da suke yi a gidajen al-umma.

Tun a farkon shekarar nan, kimanin mutane dubu 30 ne suka kauracewa gidajensu, inda suka nemi mafaka a wasu wuarare cikin kasar ta Afrika Tsakiya, yayinda da kuma, wasu dubu 20 dabam, suka shiga kasar jamhuriyyar Congo da ke da makwabataka da su, dan samun mafaka

Mai magana da yawun hukumar kula da yan gudun hijira ta majalisar dinkin duniya, Karin De Gruiji ya bayyana wa manema labarai a birnin Geneva cewa, akwai tsantsan rugujawar doka da oda a kasar Afrika ta tsakiya, kuma yawan al-ummar kasar ya ragu da kusan rabi.

Kasar dai, na fafutukar farfadowa daga matsalar da ta samu a shekara ta 2013, bayan juyin mulkin da akayiwa Francois Bozize.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.