Boko Haram ta kaiwa dakarun Cadi hari
Sojan Cadi uku ne suka mutu a wani hari da yan kungiyar Boko Haram suka kai a arewaci Kamaru a wata sanarwa daga rudunar Cadi a jiya.
Wallafawa ranar:
Harin da yan kungiyar Boko Haram suka kai ya raunata sojin Cadi 12 yayi da a cewar wanan majiya dakarun Cadi sun samu nasarar kashe mayakan na Boko Haram 123.
Dakarun Cadi sun iso arewaci Kamaru tun ranar 17 ga watan Janiru da ya shude da nufin kai dauki zuwa rudunar tsaro Kamaru wajen yakar kungiyar Boko Haram.
Cadi ta tura da kusan sojin 2500 zuwa Kamaru yayi da ake sa ran wasu daga sauren kasashen Afrika za su kasancewa a cikin wanan ruduna ta musaman domin yakar Boko Haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu