Isa ga babban shafi
Kamaru-Najeriya

Dakarun Kamaru sun ceto mutane 24 daga hannun Boko Haram

Hukumomin Kasar Kamaru sun tabbatar da ceto mutane 24 daga cikin 80 da kungiyar Boko Haram ta sace a Arewacin kasar. Wannan na zuwa ne a yayin da Chadi ke shirin kaddamar da yaki akan Mayakan.

Dakarun Kamaru da ke fada Boko Haram a arewa mai nisa
Dakarun Kamaru da ke fada Boko Haram a arewa mai nisa AFP PHOTO / REINNIER KAZE
Talla

Sojojin Kamaru sun kora Mayakan na Boko Haram zuwa Najeriya bayan kwashe lokaci suna musayar wuta da su a arewacin kasar.

Wani Sojan Kamaru ya shaidawa Kamfanin Dillacin labaran Faransa cewa ‘Yan Boko Haram sun kai hari ne a wasu kauyuka guda biyu a yankin arewa mai nisa tare da sace mutane 80. Wannan ne kuma karo na farko da Boko Haram ta sace mutane a wata kasa sabanin Najeriya.

Kasar Chadi tace zata aika da dakaru 400 da jirage masu saukar Ungulu domin yakar Boko Haram a arewacin Kamaru.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.