Isa ga babban shafi
Najeriya

Mata ne suka kai hare hare a Kano

‘Yan Sandan Jihar Kano a Najeriya sun tabbatar da cewa wasu mata guda biyu suka kai harin bama bamai a kasuwar Kantin Kwari a jiya Talata. Wannan na faruwa duka mako guda da aka kai wani kazamin hari a cikin babban Masallacin tsakiyar garin na Kano.

Jami'an tsaro a inda aka kai Harin Kano  a Masallaci
Jami'an tsaro a inda aka kai Harin Kano a Masallaci REUTERS/Stringer
Talla

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da mutuwar mutane shida inda wasu bakwai ke kwance a asibiti sanadiyar hare haren kunar bakin wake da ‘yan mata biyu suka kai.

Kungiyar agaji ta Red Cross tace mutane 10 suka dauka zuwa asibiti wadanda suka samu raunuka a sakamakon hare haren.

Shedun gani da ido sun tabbatarwa Wakilin RFI Hausa Abubakar Isa Dandago cewa Mata ne suka tayar da bom din da misalin karfe 3 na rana, lokacin da ‘Yan kasuwa ke cikin hada-hadar kasuwanci a Kantin Kwari.

01:34

Rahoton harin Kantin Kware a Kano

Abubakar Issa Dandago

Kwamishin ‘Yan Sandan Kano Adenrele Shinaba yace Mata ne suka kai hare haren sanye da Hijabi.

Bama baman dai sun tashi ne a inda ake ajiye ababen hawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.