Nijar
Birgi Rafini ya tsallake yunkurin tsige shi a Nijar
Firaminsitan Jamhuriyar Nijar Birgi Rafini, ya tsallake yunkurin da ‘yan majalisar kasar suka yi na tsige shi a cikin tsakiyar daren Laraba kamar yadda wasu ‘yan adawa 24 suka bukata. ‘Yan majalisa 105 ne ke cikin zauren lokacin jefa kuri’ar, amma bayan kammala zabe an kirga kuri’u 107, abin da ya sa shugaban riko na majalisar ya bukaci a sake jefa kuri’a karo na biyu, lamarin da ya sa ‘yan adawa suka fice daga zauren. Wakiliyar RFI Hausa a Yamai Lydia Addo ta aiko da Rahoto.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Rahoto: Birgi Rafini ya tsallake yunkurin tsige shi a Nijar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu