Isa ga babban shafi
Burkina Faso

An rantsar da Kafando a matsayin shugaban riko

Michel Kafando ya karbi rantsuwar kama aiki a matsayin sabon shugaban riko na kasar Burkina Faso, a daidai lokacin da kasashen duniya ke ci gaba da jinjina wa al’ummar kasar dangane da cim ma jituwa kan wanda zai jagoranci kasar domin dawo da ita kan turbar dimokuradiyya.

Shugaban rikon kwarya na Burkina Faso, Michel Kafando a Ouagadougou
Shugaban rikon kwarya na Burkina Faso, Michel Kafando a Ouagadougou AFP/ROMARIC HIEN
Talla

A yau Talata ne aka rantsar da Kafando domin jagorantar kasar har zuwa a gudanar da sabon zaben shugaban kasa bayan hambarar da gwamnatin Blaise Compaore.

Kafin gudanar da bikin rantsuwar, an karrama Kanal Isaac Zida shugaban Soja wanda ya amince ya mika mulki ga farar hula.

A ranar Juma’a ne Kafando zai karbi ragamar tafiyar da Burkina Faso daga hannun Kanala Zida.

Sauyin gwamnati da aka samu a Burkina Faso na zuwa kafin cikar wa’adin kungiyar Tarayyar Afrika, bayan gargadin kakabawa kasar Takunkubi idan har sojoji ba su mika mulki ga Farar hula ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.