Isa ga babban shafi
Kenya

‘Yan sandan Kenya sun wa Masallatai dirar-mikiya

Jami’an tsaron Kenya sun kaddamar da samame a wasu Masallatai da ke birnin Mombasa domin farautar Mayakan kungiyar al Shabaab. ‘Yan sandan sun kashe mutum guda a samamen da suka kaddamar da sanyin safiyar Litinin.

Jami'an tsaro a birnin Mombasa na kasar Kenya
Jami'an tsaro a birnin Mombasa na kasar Kenya REUTERS/Siegfried Modola
Talla

Jami’an tsaron sun kaddamar da samamen ne a Masallacin Musa da Sakina da ke birnin Mombasa, bayan sun samu labarin kungiyar al Shabaab na shirin kai hari a cikin kasar.

‘Yan sandan sun cafke mutane da dama, kamar yadda shugabansu Geoffrey Mayek ya tabbatar.

Tuni dai kasashen Turai suka bukaci mutanensu su kauracewa tafiya birnin Mombasa saboda barazanar tsaro.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.