Harkar fatauci tsakanin arewacin Nigeria da kasashen arewacin nahiyar Africa nada tsohon tarihi, inda tarihi ke nuna wannan harkar ta shafe darururwan shekaru ana yi. Cikin shirinmu na makon da ya gabata mun duba yadda wannan harka take a wannan zamanin, da kuma yadda matsalar tsaro ke barazana ga wannan harkar, musamman ma sakamakon hare-hare da kungiyar Boko Haram take kaiwa, a kan hanyoyin da ake bi don fataucin tsakanin Nigeria da Sudan.Cikin Shirin na wannan makon Nasiruddeen Muhammad, ya ci gaba da duba wannan lamarin, musamman yadda matsalar ke sanadiyyar karuwar farashin kayayyaki, tsakanin Nigeria da Sudan, lamarin da ke shafar sauran kasashen nahiyar Africa kamar Su Kanya, Habasha da Eritriya...ayi saurare lafiya.
Sauran kashi-kashi
-
Yadda matsin rayuwa ya tilastawa 'yan Najeriya fasa rumbunan abinci
Shirin Kasuwa akai miki dole tare da Ahmed Abba a wannan makon ya yada zango ne a Tarayyar Najeriya, inda ya yi dubi kan matsanancin kuncin rayuwar da al’umman kasar suka shiga da har ta kai ana fasa rumbunan abinci ko tare manyan motocin dakon kaya a tituna ana kwasan abinci.06/03/202410:22 -
Faduwar darajar Naira ta tsayar da harkokin 'yan canji a makwaftan Najeriya
Shirin 'Kasuwa a kai miki dole' na wannan mako ya tattauna akan yadda faduwar darajar Naira ke haddasa koma bayan kasuwar 'yan canji a makwaftan Najeriya.07/02/202410:19 -
Dalilan soke lasisin wasu kamfanonin wutar lantarki
Shirin Kasuwa a Kai Maki Dole na wannan mako, ya mayar da hankali ne a game da batun wutar lantarki a Najeriya, bangaren da ke fama da matsalololi tsawon shekaru.Shirin zai yi dubi ne a game da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na sokewa da kuma sabunta lasisi ga wasu kamfanonin da ke da alhaki rarraba wuta a cikin kasar.31/01/202410:02 -
Yadda faduwar darajar Naira ke yin illa ga kasuwanci a Najeriya
Shirin 'Kasuwa a kai miki dole' na wanna makon ya mayar da hankali akan faduwar darajar naira da ke ci gaba da yin illa ga harkokin kasuwanci a sassan Najeriya.24/01/202409:52 -
Yadda rufe iyakar Benin ya haifar da tsadar rayuwa a Nijar
Shirin "Kasuwa akai Miki dole" na wanan mako tare da Ahmed Abba ya leka ne jihar Dosso dake Jamhuriya Nijar, yankin da ke kan iyaka da birnin Cotonou na Jamhuriya Benin inda jama'a suka shiga matsanancin halin tsadar rayuwa tare da kariyar tattalin arziki, sakamakon takun-kuman da Kungiyayoyi irinsu ECOWAS ko CEDEAO suka laftawa kasar, saboda Juyin mulkin da Sojoji sukayi.22/11/202309:50