Isa ga babban shafi
EQUATORIAL GUINEE

Shugaban Equatorial Guinea yayi afuwa ga 'yan siyasar da suka fice daga kasar

Shugaban kasar Equatorial Guinea Teodoro Obiang Nguema, ya sanar da yin afuwa ga dukkanin masu adawa da shi amma suke gudun hijira a kasashen ketare. Kudurin dokar da shugaba Obiang Ingema ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa an dauki wannan mataki ne domin bai wa illahirin ‘yan siyasar kasar da ke zaune a kasashen ketare damar komawa gida, domin halartar taron mahawara kan lamurran da suka shafi kasar, wanda da za a gudanar a cikin kwanaki goman farkon watan nuwamba mai zuwa.Cikin watan Agusta, shugaba Ingema wanda ya dare kan karagar mulkin kasar tun a shekarar 1979, ya bayyana cewa za a gudanar da babban taro, da zai hada dukkanin ‘yan siyasar kasar, kuma za a bai wa wadanda ke zaune a waje damar halarta.To sai dai bayan da shugaban ya bayyana haka, da dama daga cikin manyan ‘yan siyasar kasar da ke zaune a kasashen waje, sun ce ba za su koma gida ba matukar dai ba a shelanta yin afuwa ga illahirin ‘yan siyasar da ke zaune a waje ba.Shugaban dai ya bayyana cewa wannan taro, zai kasance wata dama domin tattaunawa akan dukkanin batutuwan da suka shafi kasar. 

Shugaban kasar Equatorial Guinea, Teodoro Obiang Nguema
Shugaban kasar Equatorial Guinea, Teodoro Obiang Nguema Reuters/James Akena
Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.