Isa ga babban shafi
Kenya-Somalia

Shekara daya da kai harin Westgate a Nairobi

Yau lahadi, al’ummar kasar Kenya na juyayin cika shekara daya da harin da ‘yan bindiga suka kai wa cibiyar hada-hadar kasuwa ta Westgate da ke birnin Nairobi inda aka samu asarar rayukan mutane akalla 67 a ranar 21 ga watan satumbar bara.

Westgate, kasuwar da aka kai wa hari ranar 21 ga watan satumbar 2013 a Nairobi
Westgate, kasuwar da aka kai wa hari ranar 21 ga watan satumbar 2013 a Nairobi REUTERS/Johnson Mugo
Talla

An dai gudanar da addu’o’I a birnin Nairobi, yayin da ‘yan uwan wadanda suka rasa rayukansu suka ajiye furanni a wani na musamman da aka gina domin tunawa da mutanen da ‘yan bindiga suka kashe bayan share tsawon kwanaki 4 suna garkuwa da su a cikin wannan kasuwa.

Shugaban rundunar ‘yan sandar kasar ta Kenya David Kimaiyo, ya ce an tsaurara matakan tsaro domin kaucewa yiyuwar kai wa kasar hari a lokacin bukukuwan. An dai bayyana cewa harin na bara, magoya bayan kungiyar Alshebab da ke Somalia ne suka kai shi.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.